About Script
Surah Al-Fil ( The Elephant )

Hausa

Surah Al-Fil ( The Elephant ) - Aya count 5

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصْحَٰبِ ٱلْفِيلِ ﴿١﴾

Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba?

أَلَمْ يَجْعَلْ كَيْدَهُمْ فِى تَضْلِيلٍۢ ﴿٢﴾

Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba?

وَأَرْسَلَ عَلَيْهِمْ طَيْرًا أَبَابِيلَ ﴿٣﴾

Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.

تَرْمِيهِم بِحِجَارَةٍۢ مِّن سِجِّيلٍۢ ﴿٤﴾

Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.

فَجَعَلَهُمْ كَعَصْفٍۢ مَّأْكُولٍۭ ﴿٥﴾

Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?

Quran For All V5